Home General Na damu da batun rashin lantarki a arewa – Tinubu

Na damu da batun rashin lantarki a arewa – Tinubu

Bola Ahned Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya nuna damuwarsa kan rashin wutar lantarki da arewacin Najeriya ke ci gaba da fuskanta.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan harkar yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya fitar, ya ce abin damuwa ne matuka ganin yadda ƴan yankin ke ci gaba da kasancewa cikin duhu kuma hakan na ƙara kassara ɓangaren tattalin arziki.

Tinubu ya ce yanzu yana jagorantar ƙoƙari da ake yi wajen ganin an gyara matsalar ta rashin lantarki.

Ya buƙaci ministan lantarki da sauran hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta kammala aikin gyara turakun wuta da aka lalata da nufin mayar da wuta ga jihohin arewa.

“Ina cikin damuwa ainun kan rahotannin lalata wayoyin lantarki da sauran abubuwa da suka janyo rahin wuta,” in ji Tinubu.

Tinubu ya yi kira ga kamfanin rarraba wutar lantarki na Najeriya da su ƙoƙarta wajen ganin lantarki ta koma domin rage wa al’uma raɗadin da suke ciki.

Ya ce gwamnati ba za ta lamunci ci gaba da yin zagon ƙasa da kuma lalata turakun wutar lantarki ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp