Home General Na damu da batun rashin lantarki a arewa – Tinubu

Na damu da batun rashin lantarki a arewa – Tinubu

Bola Ahned Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya nuna damuwarsa kan rashin wutar lantarki da arewacin Najeriya ke ci gaba da fuskanta.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan harkar yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya fitar, ya ce abin damuwa ne matuka ganin yadda ƴan yankin ke ci gaba da kasancewa cikin duhu kuma hakan na ƙara kassara ɓangaren tattalin arziki.

Tinubu ya ce yanzu yana jagorantar ƙoƙari da ake yi wajen ganin an gyara matsalar ta rashin lantarki.

Ya buƙaci ministan lantarki da sauran hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta kammala aikin gyara turakun wuta da aka lalata da nufin mayar da wuta ga jihohin arewa.

“Ina cikin damuwa ainun kan rahotannin lalata wayoyin lantarki da sauran abubuwa da suka janyo rahin wuta,” in ji Tinubu.

Tinubu ya yi kira ga kamfanin rarraba wutar lantarki na Najeriya da su ƙoƙarta wajen ganin lantarki ta koma domin rage wa al’uma raɗadin da suke ciki.

Ya ce gwamnati ba za ta lamunci ci gaba da yin zagon ƙasa da kuma lalata turakun wutar lantarki ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp