Home Labarai NASSI ta bude hanyar neman Rancen Naira biliyan 75

NASSI ta bude hanyar neman Rancen Naira biliyan 75

Ƙungiyar masu ƙanana da matsakaitan Masana’antu ta Najeriya, wato Nigerian Association of Small Scale Industrialists (NASSI), ta bude hanyar neman rancen Naira Bilyan 75 da Gwamnatin Najeriya ta sahale musu.

Shugaban Kungiyar na kasa Chief Dakta Solomon Daniel Vonfa ne ya sanar da hakan, a yayin wani taron manema Labarai da ya jagoranta a Shelkwatar Kungiyar dake Babban Birnin tarayya Abuja, inda ya ce a yau suka bude shafin domin Mambobin kungiyar dama dukkan al’ummar Najeriya su nema.

Hanyar neman rancen ita ce “https://fgnboimsmeinterventionloan.boi.ng/ ” a inda wadanda zasu nema ta hannun Kungiyar kuma zasu fara yin rijista da kungiyar ta shafin “https://portal.nassi-ng.org/”.

Da yake karin haske, Babban Ma’ajin kungiyar na kasa, Dakta Abubakar Tanko Bala ya ce ga dukkan masu bukatar wannan rance zasu iya nema ta waccan hanya ko kuma su ziyarci Ofishin Kungiyar NASSI mafi kusa da shi.

Kungiyar ta kuma shawarci Mambobin ta dama dukkan al’ummar kasar da suyi amfani da wannan dama, domin bunkasa kasuwancin su dama samar karin kudin shiga ga kasar dama habbaka tattalin arzikin ta.

Taron manema Labaran ya sami halartar masu ruwa da tsakin Kungiyar na sassan Kasar dama tawagar Manyan Jami’an Bankin Masana’antu na Najeriya wato Bank of Industry, karkashin Jagorancin Hajiya Amina Habu.

A ranar 16 ga watan Oktobar nan ne Gwamnatin Najeriya ta amince da bawa mambobin kungiyar rancen Naira Bilyan 75, ta hannun Bankin Masana’antu domin su bunkasa kasuwancin su dama farfado da tattalin arzikin kasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp