Home General EFCC za ta sa ido kan kashe kuɗaɗen ƙananan hukumomi

EFCC za ta sa ido kan kashe kuɗaɗen ƙananan hukumomi

Hukumar EFCC ta ce za ta ƙarfafa bibiya tare da bin diddigin yadda ƙananan hukumomi suke kashe kuɗaɗensu a daidai lokacin da ake tunanin cin gashin kansu zai fara aiki daga watan Nuwamba, inda ake tunanin za a fara tura musu kuɗadensu kai-tsaye.

Tura kuɗaɗen kai-tsaye na cikin yunƙurin tabbatar da cin gashin kan ƙananan hukumomin guda 774 a Najeriya, lamarin da shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi na Najeriya, Hakeem Ambaliya ya bayyana wa jaridar Punch cewa suna farin ciki.

A ranar 11 ga watan Yulin bana ne dai Kotun Ƙolin Najeriya, ƙarƙashin jagorancin Mai shari’a Garba Lawal, ta yanke hukuncin cewa ba daidai ba ne gwamnoni su riƙa karɓa tare da kula da kuɗaɗen ƙananan hukumomi, inda ta buƙaci akanta-janar na ƙasar ya tabbatar ana tura wa ƙananan hukumomin kuɗaɗensu kai-tsaye.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp