Home Labarai Cire T-Gwarzo Daga Minista Babban Kuskure ne – Kungiya Matasan APC ta...

Cire T-Gwarzo Daga Minista Babban Kuskure ne – Kungiya Matasan APC ta Kasa

Kungiyar matasan jam’iyyar APC ta kasa ta kalubalanci tsige Injiniya Abdullahi Tijjani Gwarzo a matsayin karamin ministan gidaje da raya birane.

Kungiyar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da shugabanta Abdullahi Wada Kura ya sanyawa hannu kuma ta aikowa kadaura24, ta bayyana cire Gwarzo a matsayin abin mamaki da hadari ga jam’iyyar APC a jihar.

“Mafi yawan al’ummar jihar Kano sun tausayawa sakamakon cirewar da aka yi masa. Cire shi daga minista ya haifar da rashin jin dadi kuma zai kawo tsaiko ga tasirin jam’iyyar APC a jihar Kano,” a cewar kungiyar.

T Gwarzo wanda aka tsige shi da wasu mutane 4 ya godewa shugaban kasar da ya bashi damar yiwa kasarsa hidima.

Kungiyar ta yi zargin cewa wani fitaccen dan Siyasa daga jihar kano ne ya kitsa yadda aka cire T Gwarzo daga Minista.

“Wanda ya kitsa cireT Gwarzo ya yaudari shugaban kasa, kuma ya kamata ya sani mutum daya bai isa ya rika yanke shawara da sunan Kano ba,” inji kungiyar

Kungiyar ta yi gargadin cewa wannan mataki kokari ne kawai na karawa jam’iyyar NNPP karfi cikin dubarane, ganin cewa bai kamata a jefar da ’yan siyasa irinsu Gwarzo ba tare da wani kwakkwaran dalili ba.

“Idan ba a mayar da shi Kan mukaminda ba, nan da shekarar 2027, shugaban kasa zai gane ko Gwarzo na jama’a ko ba shi da su, amma ta fito filin cewa al’ummar jihar Kano suna tare da Gwarzo saboda yadda jam’a suka tausaya masa .

“Kano ta Arewa ta zamo babbar shiyyar APC ce saboda yadda Gwarzo da sauran masu ruwa da tsaki suka fito daga shiyyar, ba wai don mutum daya ba.

Ya kamata shugaban kasa ya duba amma matakin da aka dauka shawara ce mai hadari a 2027,”in ji Wanda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp