Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka mayakan Boko haram a Borno

Sojojin Nijeriya sun hallaka mayakan Boko haram a Borno

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce jiragen samanta sun kashe mayaƙan Boko Haram da dama a ranar 25 ga Oktoba a arin Bula Marwa a Borno.

Daraktan hulɗa da jama’a na rundunar, Iya Comodore, Olusola Akinboyewa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin a Abuja.

Akinboyewa ya ce sun gano Bula Marwa ne garin da Boko Haram suka taruwa, inda suka gano babura suna ta zirga-zirga, hakan ya sa aka aika jiragen sama yankin, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN ya ruwaito.

“Da isan jiragen, sai hoton da jiragen ya ɗauko ya tabbatar da taron ƴan Boko Haram a saman babura 12, inda aka bibiyi baburan zuwa wani wuri da akwai ƙarin ƴan ta’addan suke jiran zuwan su.

“Wannan ya sa jiragen suka yi ɓarin wuta a yankin, sannan daga baya jirgin ya hango ƴan ta’addan suna sake dawowa yankin domin kwashe waɗanda suka raunata.

“Wannan ya sa jiragen suka koma, suka ƙara yin luguden wuta, inda a nan ma aka sake kashe wasu ƴan ta’addan.”

Akinboyewa ya ce an sake ganin wasu tarin ƴan Boko Haram sun taru a ƙarƙashin wata bishiya, inda nan ma jiragen suka ƙara bin su, suka musu ɓarin wuta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp