Home Labarai Cire T-Gwarzo Daga Minista Babban Kuskure ne – Kungiya Matasan APC ta...

Cire T-Gwarzo Daga Minista Babban Kuskure ne – Kungiya Matasan APC ta Kasa

Kungiyar matasan jam’iyyar APC ta kasa ta kalubalanci tsige Injiniya Abdullahi Tijjani Gwarzo a matsayin karamin ministan gidaje da raya birane.

Kungiyar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da shugabanta Abdullahi Wada Kura ya sanyawa hannu kuma ta aikowa kadaura24, ta bayyana cire Gwarzo a matsayin abin mamaki da hadari ga jam’iyyar APC a jihar.

“Mafi yawan al’ummar jihar Kano sun tausayawa sakamakon cirewar da aka yi masa. Cire shi daga minista ya haifar da rashin jin dadi kuma zai kawo tsaiko ga tasirin jam’iyyar APC a jihar Kano,” a cewar kungiyar.

T Gwarzo wanda aka tsige shi da wasu mutane 4 ya godewa shugaban kasar da ya bashi damar yiwa kasarsa hidima.

Kungiyar ta yi zargin cewa wani fitaccen dan Siyasa daga jihar kano ne ya kitsa yadda aka cire T Gwarzo daga Minista.

“Wanda ya kitsa cireT Gwarzo ya yaudari shugaban kasa, kuma ya kamata ya sani mutum daya bai isa ya rika yanke shawara da sunan Kano ba,” inji kungiyar

Kungiyar ta yi gargadin cewa wannan mataki kokari ne kawai na karawa jam’iyyar NNPP karfi cikin dubarane, ganin cewa bai kamata a jefar da ’yan siyasa irinsu Gwarzo ba tare da wani kwakkwaran dalili ba.

“Idan ba a mayar da shi Kan mukaminda ba, nan da shekarar 2027, shugaban kasa zai gane ko Gwarzo na jama’a ko ba shi da su, amma ta fito filin cewa al’ummar jihar Kano suna tare da Gwarzo saboda yadda jam’a suka tausaya masa .

“Kano ta Arewa ta zamo babbar shiyyar APC ce saboda yadda Gwarzo da sauran masu ruwa da tsaki suka fito daga shiyyar, ba wai don mutum daya ba.

Ya kamata shugaban kasa ya duba amma matakin da aka dauka shawara ce mai hadari a 2027,”in ji Wanda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp