Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka mayakan Boko haram a Borno

Sojojin Nijeriya sun hallaka mayakan Boko haram a Borno

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce jiragen samanta sun kashe mayaƙan Boko Haram da dama a ranar 25 ga Oktoba a arin Bula Marwa a Borno.

Daraktan hulɗa da jama’a na rundunar, Iya Comodore, Olusola Akinboyewa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin a Abuja.

Akinboyewa ya ce sun gano Bula Marwa ne garin da Boko Haram suka taruwa, inda suka gano babura suna ta zirga-zirga, hakan ya sa aka aika jiragen sama yankin, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN ya ruwaito.

“Da isan jiragen, sai hoton da jiragen ya ɗauko ya tabbatar da taron ƴan Boko Haram a saman babura 12, inda aka bibiyi baburan zuwa wani wuri da akwai ƙarin ƴan ta’addan suke jiran zuwan su.

“Wannan ya sa jiragen suka yi ɓarin wuta a yankin, sannan daga baya jirgin ya hango ƴan ta’addan suna sake dawowa yankin domin kwashe waɗanda suka raunata.

“Wannan ya sa jiragen suka koma, suka ƙara yin luguden wuta, inda a nan ma aka sake kashe wasu ƴan ta’addan.”

Akinboyewa ya ce an sake ganin wasu tarin ƴan Boko Haram sun taru a ƙarƙashin wata bishiya, inda nan ma jiragen suka ƙara bin su, suka musu ɓarin wuta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp