Home General NNPLC ya sake kara farashin Man Fetur a Najeriya

NNPLC ya sake kara farashin Man Fetur a Najeriya

A karo na biyu kamfanin man Fetur na Nijeriya ya sake kara kudin Man abin da ya haifar da kace nace da mamaki bayan karin da yazo a ba zata ranar Talata 29 ga Oktoba 2024, wanda wannan shine Karo na biyu da kamfanin yayi ƙari cikin makonni uku.

Kamfanin man na kasa ya kara farashin daga naira 1,030 zuwa 1060 a Babban Birnin Tarayya Abuja, yayin da a Jihar Legas farashin ya koma Naira 1,025 daga 998 a kowacce lita.

Kafin wannan ƙarin, ana sayar da litar man fetur ne a  kan N897 a Abuja, a Legas kuma N885, amma a ranar 9 ga watan Oktoba da muke bankwana da shi aka ƙara na Legas zuwa N998, na Abuja kuma zuwa N1,030.

Ķarin kudin na zuwa ne duk da fara aikin Matatar Man Ɗangote, wadda ake tunanin za ta kawo sauki da wadatuwar man a ƙasar.

Tun bayan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanar da janye Tallafin mai a watan mayun 2023, NNPCL ya ƙara kudin fetir daga 184 zuwa 1,025 a Jihar Legas.

Masana dai na ganin wannan wani mataki ne da zai kara jefa yan Najeriya cikin mawuyacin hali, dama tuni wasu suka ajiye ababen hawan su saboda tsadar farashin man.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp