Home General Gwamnatin Najeriya ta kwace kwangilar hanyar Abuja-Kaduna daga hannun kamfanin Julius Berger

Gwamnatin Najeriya ta kwace kwangilar hanyar Abuja-Kaduna daga hannun kamfanin Julius Berger

Gwamnatin Najeriya ta sanar da kawo ƙarshen yarjejeniyar aikin hanyar da ta tashi daga Abuja zuwa Kaduna da ta ƙulla da kamfanin Julius Berger.

Bayan cikar wa’adin kwanaki 14 da gwamnatin ta baiwa kamfanin na ɗaukar mataki kan tafiyar wahainiya da aikin ke yi, a yanzu ta sanar da ficewa daga yarjejeniyar ba tare da samun damar yin wata tattaunawa ba.

Ta cikin sanarwar da ma’aikatar ayyukan ta fitar mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labaranta Mohammed Ahmed ta ce an shafe watanni 13 a jere ana tattaunawa da kamfanin amma an kasa cimma matsaya, don haka babu wani zabi da ya wuce kawo ƙarshen yarjejeniyar.

Baya ga  tafiyar wahainiya da aikin ke yi, ana kuma zargin sa da ƙin bada cikakken bayani kan kuɗin da aikin ya laƙume kawo yanzu, ƙin biyayya ga dokokin da aka shimfida, da kuma ƙin biyayya ga shawarwarin da ma’aikatar ayyuka ta bashi.

RFI ta ruwaito cewa an shafe tsahon watanni ana yamutsa gashin baki tsakanin kamfani da gwamnati kan waɗannan matsaloli da suka ƙi ci suka ƙi cinyewa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp