Home General Majilisar Jihar Niger ta karyata Sojojin Nijeriya

Majilisar Jihar Niger ta karyata Sojojin Nijeriya

‘Yan bindiga dake jihar Niger a tsakiyar Nijeriya sun yi awon gaba da mutane a 20 a cikin motoci 5 da suka tare a hanyar Mariga-Kontagora.

kakakin majalisar jihar Niger, dan majalisa mai wakiltar mazabar mariga Barister Abdulmalik Sarkin-Daji ne ya tabbatar da hakan yayin da yake ganawa da manema labarai.

yace labarin ya faru ne a ranar alhamis yayin da ‘yan bindigar suka tare hanyar Mariga-kontagora tsakanin Babban-Lamba da Beri.

wannan dai jawabi na kakakin majalisar na matsayin martani ga rundunar sojojin Nijeriya, wadda ta musanta cewa ‘yan ta’addan basu mamaye wajen horar da dakarunta dake karamar hukumar Kontagora ba wanda yanzu haka sun fafadada zuwa karamar hukumar Mariga.

sarkin daji yace iyalen wadanda aka yi garkuwa da su, sun sha kai kudin fansa ga ‘yan ta’addan, wanda kuma wajen horar da dakarun sojojin Najeriya ne wajen da ake kai kudin fansar.

yace wadanda aka sako din sun bayyanawa iyalen su cewa, an ajje su ne a dajin da babub nesa da barikin sojoji ta Kontagora.

haka kuma ya kara da cewa Fasinjojin da ‘yan ta’addan suka kama ranar alhamis sun kai su ne zuwa wannan daji, in da ya bukaci dakarun sojojin sun sami bayani na gaskiya domin su fitar da ‘yan bindigar daga cikin daji.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp