Home General Jam’iyyun sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya a zaɓen gwamnan Ondo

Jam’iyyun sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya a zaɓen gwamnan Ondo

Jam’iyyun siyasa da ‘yan takara sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a zaɓen gwamnan jihar Ondo da ke kudu maso yammacin Najeriya.

An yi bikin sanya hannun ne ƙarƙashin jagorancin kwamitin zaman lafiya na ƙasa NPC, a cibiyar raya al’adu da ke Akure, babban birni jihar.

Shugaban kwamitin, Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya, ya yi kira ga duka masu ruwa da tsaki su tabbatar an gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali.

Ya kuma buƙaci shugabannin jam’iyyu da ‘yan takara su amince da sakamakon zaɓen matsawar an gudanar da shi cikin kwanciyar hankali da lumana.

A nasa ɓangare shugaban hukumar zaɓen kasar, Farfesa Mahmood Yakubu ya yaba wa kwamitin bisa ƙoƙarinsa na haɗa kan jam’iyyun da ‘yan takara a teburin yarjejeniyar zaman lafiya a lokutan zaɓukan ƙasar.

Farfesa Yakubu ya kuma yi kira ga shugabannin addinai da sarakuna da jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki su haɗa hannu da hukumarsa don gudanar da zaɓen gwamnan jihar cikin kwanciyar hankali da lumana.

A ranar 16 ga watan Nuwamban da muke ciki ne za a gudanar da zaɓen gwamnan jihar ta Ondo.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp