Home General Dalilin Gwamnatin Kano na fara kamen kananan yaran dake yawo a titi

Dalilin Gwamnatin Kano na fara kamen kananan yaran dake yawo a titi

Gwamnatin jihar Kano ta ƙaddamar da wani kwamiti da zai yi aiki kwashe yaran da ke gararamba a titunan birnin.

Hukumomi sun ce ɗaukar matakin ya zama wajibi kasancewar barin yara ƙanana suna yawo a tituna babbar barazana ce ga tsaro da kuma ci gaba al’umma.

Kwamitin zai kuma bai wa gwamnati shawarar kan yadda za a mayar da yaran garuruwan da suka fito.

Kwamitin ƙarkashin shugabancin kwamandan hukumar Hisba, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa zai bi diddigi tare da zaƙulo yaran da suke yawo a kwararo da tituna suna kwana a kasuwanni da ƙarƙashin gada a sassan birnin Kano domin samar musu da kyakkyawar makoma da kuma maslahar al’umma.

“Yaran da za mu fara kamawa sune waɗanda suke kamar an zubar da su yawo kan titi, waɗanda ba su da wata makoma, mafi yawansu ba a san daga inda suke ba. Waɗansu ‘yan Kano ne wasu yan wasu jihohin wasu kuma ‘yan wajen ƙasar nan ne ma,” in ji Ɗaurawa

“Wasunsu rayuwa ce ta yi musu tsauri ta gagara suka koma kwana ƙarƙashin gada da gareji da wajen tuburan masu shayi. Irin waɗannan yaran mai girma gwamna ke fatan a kama a tantance na gida da na wajen a san matakin da za a ɗauka a kansu.

“A basu tarbiyya a mayar da su cikin al’umma domin su zama masu amfani ka da su zama barazana ga al’umma,” in ji Malam Aminu Daurawa.

Wannan kwamitin dai ya ƙunshi wasu ƙananan kwamitoci waɗanda za su yi aikin tantance yaran ta fuskar lafiya da sauran bayanai.

Sheik Daurawa ya ce ba za a faɗi yaushe za a fara wannan aiki ba domin ka da waɗanda ake son a taimakawa su tsere a gaza cimma manufar aikin.

“An bamu filin sansanin alhazai da ke kusa da filin jirgin sama, a nan za mu ajiye su tsawon makonni biyu mu tantance su da lafiyarsu da kuma garuruwansu.

“Za a yi aikin nan ne ƙarƙashin kwamiti guda huɗu da za su kammala aikinsu cikin kwana 14 sannan gwamna ya bayyana mataki na gaba,” in ji Malam Aminu Daurawa.

To sai dai ‘yan kungiyoyin da ake aikin kare kananan yara na ganin akwai bukatar gwamnati ta lura da wasu mahimman abubuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp