Home General Mayaƙan ISWAP sun kashe sojojin Najeriya 5 a wani hari da suka...

Mayaƙan ISWAP sun kashe sojojin Najeriya 5 a wani hari da suka kai ƙarshen mako

Sojojin Najeriya biyar aka kashe wasu sama da 10 suka samu raunuka, a wani hari da mayakan ƙungiyar masu tada kayar baya suka kai wani sansanin sojoji da ke kusa da iyakar ƙasar da jamhuriyar Nijar.

A cewar wasu jami’an sojoji biyu da suka nemi a sakaya sunansu, sun shaidawa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP cewa, a ranar Asabar ne maharan da suka fito daga ƙungiyar ISWAP sun kai harin sansanin sojin da ke garin Kareto na jihar Borno.

“Mun rasa sojojinmu 5 a musayar wuta wasu 10 sun samu rauni, 4 daga cikin jami’anmu kuma sun ɓace muna ci gaba da nemansu”.

Haka nan ɗayar majiyar, ta ce ƴan bindigar sun kuma tafi da wasu manyan motocinsu huɗu da ke ɗauke da bindigogin kakkaɓo jiragen sama, tare da kona wasu motoci biyar.

Dama dai a cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta ISWAP ta fitar a jiya Lahadi, da aka wallafa a shafin SITE da ke bibiyar harkokin ƙungiyoyin ƴan ta’adda, ta yi iƙirarin kashe sojoji sama da 20 a wani harin ƙunar baƙin wake da taka kai da wata mota, sannan ta kuma ce ta kona wani sansanin soji da motocinsu 14.

Garin Kareto da ke da nisan kilomita 153 daga birnin Maiduguri fadar gwamnatin jihar Borno, nan ne bataliya ta 149 ta sojojin Najeriya da ke yaki da mayaƙan ISWAP da Boko Haram ta ke.

An kuma ɗauki tsawon lokaci mayaƙan ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi na yunkurin kai wa wurin hari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp