Home General Ƴanbindiga sun cinna wa gonaki wuta a jihar Zamfara

Ƴanbindiga sun cinna wa gonaki wuta a jihar Zamfara

Wasu da ake zargin ƴanbindiga ne sun cinna wa gonakin manoma da dama wuta tare da yin garkuwa da mutane da dama a wasu ƙauyukan jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya

Maharan sun fara kai harin ne a garin Farin Ruwa da ke ƙaramar hukumar Maru da ke a jihar ta Zamfara, inda suka kone gonakin manoma.

Sun kuma kai irin wannan harin a ƙayukan Wanke da kuma Zargada inda suka ƙone amfanin gona.

Mazauna yankunan da ke iyaka da jihar Kebbi, sun ce ƴanbindigar sun sa sun tafka gagarumar hasarar amfanin gonar da suka noma da ya hada da masara da auduga, da wake da sauran su.

Maharan sun zo ne gungu-gungu tare da cinna wa gonakin masara da wake da dawa wuta, abin da kuma ya haifar da hasara mai ɗimbin yawa.

Sun kuma yi awon gaba da dimbin mutane inda suka ƙona gonaki da dama, kamar yadda wasu daga cikin manoman da suka tafka asarar suka shaida wa BBC.

“Muna cikin ƙunci da wahala, kodayaushe idan ba a kai farmaki ba to za a kashe, akwai matsala.”

Rahotani na cewa garuruwan Wanke da Zargada da Dan Godabe na daga cikin wadanda maharan suka addaba.

Wani da ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya ce matakin da ‘yan bindigar suka dauka na kone gonaki da garkuwa da mutane domin neman kudin fansa, ya sa suna ganin kansu tamkar ba ƴan Najeriya ba.

Ya kuma yi zargin an kyale maharan na cin karensu babu babbaka, kuma babu abin da za su yi face zura ido ga kangin bautar da maharan suka saka su.

“Mutum ma bai sani ba sai ya je gonarsa ya iske ta bushe, sai mutum ya iske bala’in da ya iske sai dai kawai ya yi Kalmar Shahada,”

Sun kuma yi garkuwa da mutum bakwai bayan sun ƙona mana gonaki,” in ji wani mazauni yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 
X whatsapp