Home General Ƴanbindiga sun cinna wa gonaki wuta a jihar Zamfara

Ƴanbindiga sun cinna wa gonaki wuta a jihar Zamfara

Wasu da ake zargin ƴanbindiga ne sun cinna wa gonakin manoma da dama wuta tare da yin garkuwa da mutane da dama a wasu ƙauyukan jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya

Maharan sun fara kai harin ne a garin Farin Ruwa da ke ƙaramar hukumar Maru da ke a jihar ta Zamfara, inda suka kone gonakin manoma.

Sun kuma kai irin wannan harin a ƙayukan Wanke da kuma Zargada inda suka ƙone amfanin gona.

Mazauna yankunan da ke iyaka da jihar Kebbi, sun ce ƴanbindigar sun sa sun tafka gagarumar hasarar amfanin gonar da suka noma da ya hada da masara da auduga, da wake da sauran su.

Maharan sun zo ne gungu-gungu tare da cinna wa gonakin masara da wake da dawa wuta, abin da kuma ya haifar da hasara mai ɗimbin yawa.

Sun kuma yi awon gaba da dimbin mutane inda suka ƙona gonaki da dama, kamar yadda wasu daga cikin manoman da suka tafka asarar suka shaida wa BBC.

“Muna cikin ƙunci da wahala, kodayaushe idan ba a kai farmaki ba to za a kashe, akwai matsala.”

Rahotani na cewa garuruwan Wanke da Zargada da Dan Godabe na daga cikin wadanda maharan suka addaba.

Wani da ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya ce matakin da ‘yan bindigar suka dauka na kone gonaki da garkuwa da mutane domin neman kudin fansa, ya sa suna ganin kansu tamkar ba ƴan Najeriya ba.

Ya kuma yi zargin an kyale maharan na cin karensu babu babbaka, kuma babu abin da za su yi face zura ido ga kangin bautar da maharan suka saka su.

“Mutum ma bai sani ba sai ya je gonarsa ya iske ta bushe, sai mutum ya iske bala’in da ya iske sai dai kawai ya yi Kalmar Shahada,”

Sun kuma yi garkuwa da mutum bakwai bayan sun ƙona mana gonaki,” in ji wani mazauni yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp