Home General Mayaƙan ISWAP sun kashe sojojin Najeriya 5 a wani hari da suka...

Mayaƙan ISWAP sun kashe sojojin Najeriya 5 a wani hari da suka kai ƙarshen mako

Sojojin Najeriya biyar aka kashe wasu sama da 10 suka samu raunuka, a wani hari da mayakan ƙungiyar masu tada kayar baya suka kai wani sansanin sojoji da ke kusa da iyakar ƙasar da jamhuriyar Nijar.

A cewar wasu jami’an sojoji biyu da suka nemi a sakaya sunansu, sun shaidawa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP cewa, a ranar Asabar ne maharan da suka fito daga ƙungiyar ISWAP sun kai harin sansanin sojin da ke garin Kareto na jihar Borno.

“Mun rasa sojojinmu 5 a musayar wuta wasu 10 sun samu rauni, 4 daga cikin jami’anmu kuma sun ɓace muna ci gaba da nemansu”.

Haka nan ɗayar majiyar, ta ce ƴan bindigar sun kuma tafi da wasu manyan motocinsu huɗu da ke ɗauke da bindigogin kakkaɓo jiragen sama, tare da kona wasu motoci biyar.

Dama dai a cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta ISWAP ta fitar a jiya Lahadi, da aka wallafa a shafin SITE da ke bibiyar harkokin ƙungiyoyin ƴan ta’adda, ta yi iƙirarin kashe sojoji sama da 20 a wani harin ƙunar baƙin wake da taka kai da wata mota, sannan ta kuma ce ta kona wani sansanin soji da motocinsu 14.

Garin Kareto da ke da nisan kilomita 153 daga birnin Maiduguri fadar gwamnatin jihar Borno, nan ne bataliya ta 149 ta sojojin Najeriya da ke yaki da mayaƙan ISWAP da Boko Haram ta ke.

An kuma ɗauki tsawon lokaci mayaƙan ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi na yunkurin kai wa wurin hari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp