Home General Mayaƙan ISWAP sun kashe sojojin Najeriya 5 a wani hari da suka...

Mayaƙan ISWAP sun kashe sojojin Najeriya 5 a wani hari da suka kai ƙarshen mako

Sojojin Najeriya biyar aka kashe wasu sama da 10 suka samu raunuka, a wani hari da mayakan ƙungiyar masu tada kayar baya suka kai wani sansanin sojoji da ke kusa da iyakar ƙasar da jamhuriyar Nijar.

A cewar wasu jami’an sojoji biyu da suka nemi a sakaya sunansu, sun shaidawa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP cewa, a ranar Asabar ne maharan da suka fito daga ƙungiyar ISWAP sun kai harin sansanin sojin da ke garin Kareto na jihar Borno.

“Mun rasa sojojinmu 5 a musayar wuta wasu 10 sun samu rauni, 4 daga cikin jami’anmu kuma sun ɓace muna ci gaba da nemansu”.

Haka nan ɗayar majiyar, ta ce ƴan bindigar sun kuma tafi da wasu manyan motocinsu huɗu da ke ɗauke da bindigogin kakkaɓo jiragen sama, tare da kona wasu motoci biyar.

Dama dai a cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta ISWAP ta fitar a jiya Lahadi, da aka wallafa a shafin SITE da ke bibiyar harkokin ƙungiyoyin ƴan ta’adda, ta yi iƙirarin kashe sojoji sama da 20 a wani harin ƙunar baƙin wake da taka kai da wata mota, sannan ta kuma ce ta kona wani sansanin soji da motocinsu 14.

Garin Kareto da ke da nisan kilomita 153 daga birnin Maiduguri fadar gwamnatin jihar Borno, nan ne bataliya ta 149 ta sojojin Najeriya da ke yaki da mayaƙan ISWAP da Boko Haram ta ke.

An kuma ɗauki tsawon lokaci mayaƙan ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi na yunkurin kai wa wurin hari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp