Home General PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen jihar Ondo

PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen jihar Ondo

Jam’iyyar PDP ta yi watsi da sakamakon zaben jihar Ondo, bayan hukumar zaɓe mai zaman kanta INEC ta ayyana ɗan takarar jam’iyyar APC, Gwamna Lucky Aiyedatiwa a matsayin wanda ya lashe zaben.

PDP ta ce za ta garzaya kotu domin ƙalubalantar sakamakon zaɓen da aka gudanar a ranar Asabar.

Muƙaddashin hulda da manema labarai na Jam’iyyar PDP ya yi zargin cewa an tafka magudi da amfani da karfin tsiya aka kada dan takararsu Mr. Agboola Ajayi.

Hakan na zuwa ne bayan wasu korafe-korafe da wakilin jam’iyyar PDP na karamar hukumar Idanre ya yi zargin cewa ba a yi zabe a unguwar Ofosun Oniseri ba, yayin da aka kori ƴan PDP, aka ƙwace ƙuri’u a Alade.

Alhaji Abdullahi Ibrahim ya yi zargin cewa zaben ya saɓa wa tsarin dimokuradiyya inda ya ce za su dauki mataki na gaba.

“Za mu garzaya kotu a matsayinmu na jam’iya, da muke sukar lamirin wannan zaɓe, mun yi tir da Allah wadai da hukuncin da hukumar zaɓe ta bayar.”

Tuni jam’iyyar PDP ta ce za ta yi nazari kan zaben da kuma sakamakonsa kafin ɗaukar mataki na gaba kan abin da ta kira kare dimokuraɗiyya a Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp