Home General Yau za a fara allurar rigakafin ƙyandar biri a Najeriya

Yau za a fara allurar rigakafin ƙyandar biri a Najeriya

A yau Litinin ne za a fara allurar riga-kafin ƙyandar biri a wasu jihohi bakwai a Najeriya., wanda hakan zai sa ƙasar ta zama ta uku da za ta yi riga-kafin bayan Rwanda da Jamhuriyar Dumukuraɗiyyar Kongo.

Wannan shi ne karon farko da Najeriya za ta yi riga-kafin a kan cutar ta ƙyandar biri bayan ɓarkewarta.

Ma’aikatar lafiya ta ƙasar ta ce za a fi mayar da hankali ne a kan ma’iakatan lafiya da sauran rukunan jama’a da ke cikin haɗarin kamuwa da cutar.

A watan Agusta Najeriya ta karɓi allurarn riga-kafin na farko da aka bai wa Afirka, wanda kuma a wannan watan ne hukumar lafiya ta duniya ta ayyana cutar a matsayin annoba ta duniya

Amurka ta bai wa Najeriya kwalaban allurar sanfurin Jynneos (MVA), 10,000.

Tun daga farkon shekarar nan rahotanni sun tabbatar da mutum 118 a jihohi 28 daga cikin 36, da kuma Abuja. ne suka kamu da cutar a Najeriya, kamar yadda hukumar lafiya ta duniya, WHO ta sanar.

Hukumar yaki da bazuwar cutuka ta Najeriya ta ce, zuwa yanzu a wannan shekara daga watan Oktoba, 27, akwai mutane 1,442 da ake zargin sun kamu da cutar daga jihohi 36 da kuma Abuja.

Kasashen Afirka 20 sun tabbatar da bullar cutar a kasarsu a wannan shekara, kuma aranar Asabar ne Angola ta bayar da rahoton mutum na farko da ta tabbatar ya kamu a kasarta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp