Home General Najeriya ta roƙi Chadi kada ta janye daga rundunar ƙasashe ta yaƙi...

Najeriya ta roƙi Chadi kada ta janye daga rundunar ƙasashe ta yaƙi da Boko Haram

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya tura wata tawaga mai ƙarfin gaske zuwa N’Djamena, babban birnin Chadi bayan da Shugaban Chadin ya yi barazanar janye dakarun ƙasarsa daga rundunar haɗaka ta yaƙi da ‘yanta’adda a yankin Sahel.

A jiya Lahadi ne tawagar ta Najeriya ta je N’Djamena, inda a can hedikwatar rundunar (MNJTF), da ta ƙunshi dakarun Najeriya da Nijar da Chadi da Kamaru da Jamhuriyar Benin, take.

Shugaba Deby ya yi barazanar janye sojojin ƙasarsa ne bayan da mayaƙan da ake zargi na ƙungiyar Boko Haram ne suka kashe dakarun ƙasarsa 40 a tsibirin Barkaram, da ke yankin tafkin Chadi a ranar 27 ga watan Oktoba.

Saboda wannan barazana ne shugaban na Najeriya ya tura tawagar ƙarƙashin jagorancin mai ba shi shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, domin tattauna batun haɗin kan tsaron.

Rahotanni sun ce, bayan gabatar da ta’aziyyar Shugaba Tinubu ga Shugaban na Chadi kan rasa sojojin, tawagar ta tabbatar wa da shugaban na Chadi samun cikakken goyon bayan Najeriya wajen yaƙi da ta’addanci.

Babban hafsan hafsoshin Najeriya Janar Christopher Musa, wanda shi ma yake cikin tawagar ya ce ƙudurin sojin ƙasashen biyu zai tabatar da nasarar yaƙi da ‘yanta’adda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp