Home General PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen jihar Ondo

PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen jihar Ondo

Jam’iyyar PDP ta yi watsi da sakamakon zaben jihar Ondo, bayan hukumar zaɓe mai zaman kanta INEC ta ayyana ɗan takarar jam’iyyar APC, Gwamna Lucky Aiyedatiwa a matsayin wanda ya lashe zaben.

PDP ta ce za ta garzaya kotu domin ƙalubalantar sakamakon zaɓen da aka gudanar a ranar Asabar.

Muƙaddashin hulda da manema labarai na Jam’iyyar PDP ya yi zargin cewa an tafka magudi da amfani da karfin tsiya aka kada dan takararsu Mr. Agboola Ajayi.

Hakan na zuwa ne bayan wasu korafe-korafe da wakilin jam’iyyar PDP na karamar hukumar Idanre ya yi zargin cewa ba a yi zabe a unguwar Ofosun Oniseri ba, yayin da aka kori ƴan PDP, aka ƙwace ƙuri’u a Alade.

Alhaji Abdullahi Ibrahim ya yi zargin cewa zaben ya saɓa wa tsarin dimokuradiyya inda ya ce za su dauki mataki na gaba.

“Za mu garzaya kotu a matsayinmu na jam’iya, da muke sukar lamirin wannan zaɓe, mun yi tir da Allah wadai da hukuncin da hukumar zaɓe ta bayar.”

Tuni jam’iyyar PDP ta ce za ta yi nazari kan zaben da kuma sakamakonsa kafin ɗaukar mataki na gaba kan abin da ta kira kare dimokuraɗiyya a Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp