Kwalara ta kashe mutum 25 a jihar Sokoto – Kwamishina

Aƙalla mutum 25 ne suka mutum aka kwantar da wasu da dama kuma a asibitoci sakamakon ɓarkewar cutar kwalara – amai da gudawa – a ƙananan hukumomi uku a jihar Sokoto.

Kwamishinar lafiya ta jihar Asabe Balarabe wadda ta bayyana haka ga manema labaraai a Sokoto, ta ce ana yi wa mutum 15 da suka kamu da cutar daga yankunan ƙaramar hukumar Sokoto ta Arewa da Silame da kuma Kware, magani.

Asabe ta kuma ce annobar ta kama mutum 1,160 ne kuma tuni 25 sun rasu a sakamakon cutar.

Kwamishinar wadda ta ce tuni an raba magunguna a ƙananan hukumomi 18 ta ce kwamitocin taimakon gaggawa na jihar na aiki tuƙuru tare da gwamnatin jiha domin dakatar da bazuwar cutar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1465 days 11 hours 28 minutes 55 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1447 days 13 hours 10 minutes 20 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com