Home General Ƴan Boko Haram sun kashe sojoji a Borno

Ƴan Boko Haram sun kashe sojoji a Borno

Ƴan Boko Haram sun kai hari a wani sansanin sojoji da ke Borno, inda suka kashe wasu sojoji, sannan ake tunanin sun yi awon gaba da wasu makamai.

Wata majiya ce ta tabbatar wa tashar Channels aukuwar lamarin, inda ta ce mayaƙan Boko Haram na ɓangaren IS ne suka kai farmakin a sansanin soji da ke garin Kareto a ranar Asabar.

Majiya ta ce an kashe kusan sojoji 20, amma hedkwatar tsaro ta Najeriya ta ce sojoji biyar aka kashe mata a harin.

Sai dai majiyar ta ƙara da cewa an gwabza yaƙi sosai tsakanin ƴan Boko Haram ɗin da sojoji, sannan wani ɗan ƙunar bakin wake ya tayar da motar da yake ciki, wanda a ƙarshe ƴan Boko Haram ɗin suka ƙona motocin sojoji 14.

A nata ɓangaren, gwamnatin jihar Borno ta yi sojojin Najeriya jaje bisa rasa jami’anta a garin na Kareto.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp