Home General Hukumar Hisbah a Kano za ta ci gaba da rufe shagunan caca...

Hukumar Hisbah a Kano za ta ci gaba da rufe shagunan caca a jihar

Hukumar Hisbah ta jihar Kano a Najeriya ta ce za ta ci gaba da bin tsarinta na rufe shagunan masu caca bayan hukunci wata kotu.

A ranar Juma’a kotun ƙolin ƙasar ta rushe dokar 2005, da ta amince da kafa hukumar kula da caca tare da halasta cacar wasanni a ƙasar.

Kotun ta ce hukuncin na nufin gwamnatocin jihohi ne ke da wuƙa da nama game da dokokin da suka shafi caca.

Daraktan hukumar Hisbah na jihar Kanon, Dakta Abba Sufi ya ce hukuncin kotun na nufin hukumarsu za ta ci gaba da kai samame tare da rufe shagunan caca a faɗin jihar, saboda haramcin sana’ar a ƙarƙashin dokokin Musulunci.

Abba Sufi ya ce iyayen yara na yawan ƙorafi game da yadda yaransu ke ci gaba da faɗawa komar wannan mummunar sana’a a daidai lokacin da matsin rayuwa da talauci ke ƙaruwa tsakanin al’umma.

Jihar Kano na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya da ake amfani da dokokin addinin Musulunci baya da dokokin ƙasa.

A watan da ya gabata hukumar Hisbar jihar ta kai samame tare da rufe gomman shagunan caca a faɗin birnin Kano.

To sai dai an dakatar da samamen sakamakon ƙarar da wasu ƙungiyoyi suka shigar, dogaro da cewa caca ba laifi ba ne a ƙarƙashin dokokin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp