Home General Tinubu na ganawa da shugaban Faransa a birnin Paris

Tinubu na ganawa da shugaban Faransa a birnin Paris

Shugaban Najeriya na yin wata ganawa da shugaban ƙasar Faransa Emmanuel Macron a ranar farko ta ziyarar aiki da shugaban na Najeriya ke yi a ƙasar.

A yau Alhamis, Tinubu ya isa fadar shugaban Faransa ta Elysee tare da tawagarsa, wadda ta hada da ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tugga da ministan kuɗi, Wale Edun da na tsaro Badaru Abubakar.

A ɓangare ɗaya shugaban Faransa ya shiga ɗakin taron ne tare da ƙaramin ministan harkokin waje na ƙasar, Thani Mohamed Soilihi da kuma ministan tsaro na Faransa, Sebastien Lecornu da sauran jami’ai.

Ana sa ran Najeriya da Faransa za su ƙulla hulɗoɗi na diflomasiyya da kasuwanci a lokacin ziyarar ta shugaba Tinubu, wadda take zuwa bayan ragin tagomashi da Faransa take samu a Afirka.

Dangantaka ta yi tsami tsakanin Faransa da ƙasashen da ta rena a yammacin Afirka, kamar Nijar da Burkin Faso da Mali.

Ƙasashen sun yanke huldar diflomasiyya da Yamma tare da karkata akalarsu zuwa ɓangaren Rasha.

A matsayinsa na shugaban ƙungiyar ƙasashen yammacin Afirka, Tinubu ya yi ƙoƙarin ganin ƙasashen Nijar da Mali da Bukina Faso sun koma tafarkin dimokuraɗiyya sai dai har yanzu abin ya ci tura.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp