An sake zaɓar Okonjo-Iweala shugabar WTO a wa’adi na biyu

Ƙungiyar Cinikayya ta Duniya, WTO ta sake zaɓar Dakta Ngozi Okonjo-Iweala a matsayin shugabanta a wa’adin mulki na biyu, inda za ta ci gaba da jagorantar ƙungiyar har zuwa 2029.

Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da harkokin cinikayyar duniya ke cikin wani mawuyacin yanayi.

A farkon makon nan zaɓaɓɓen shugaban Amurka, Donald Trump ya ce zai ƙaƙaba sabbin haraje-harajen cinikayya da ƙasashen Canada da Mexico da China idan ya kama aiki cikin watan Janairu.

A lokacin wa’adin mulkinsa na farko, Donald Trump ya yi yunƙurin hana Ms Okonjo-Iweala samun matsayin, inda ta samu nasarar ɗarewa muƙamin bayan Joe Biden ya zama shugaban Amurka.

Babban abin tambaya a yanzu shi ne irin tasirin da ƙungiyoyin kasuwanci irin WTO za su yi, a daidai lokacin da manyan ƙasashe mafiya ƙarfin tattalin arziki ke ƙara samun saɓanin kasuwanci.

Ga kuma batun yaƙin Ukraine da ya haifar da ƙarin takunkuman kasuwancin tsakanin wasu manyan ƙasashe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com