Nijeriya da Afirka ta kudu sun sake kulla kyakkayawar alaka

kasashen Najeriya da Afirka ta kudu sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyin haɗin gwiwa a ɓangaren kasuwanci, tattalin arziƙi da kuma tsaro, inda shugaba Cyril Ramaphosa ya amince da fara bai wa ƴan Najeriya musamman ƴan kasuwa damar samun bizar ƙasar ta shekaru 5, ba tare da nuna fasfo ba.

Ramaphosa ya bayyana wannan mataki a matsayin wani ɓangare na ƙara ƙarfafa alaƙa tsakanin Najeriya da Afrika ta Kudu, lokacin buɗe taron hukumar haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da Afirka ta Kudu karo na 11 a birnin Cape Town na ƙasar .

Shugaba Ramaphosa ya ce hakan zai sauƙaƙa tafiye-tafiyen ƴan kasuwa da masu yawon buɗe ido zuwa ƙasar, ta hanyar samun bizar shekaru 5 fiye da sau 1.

Cyril ya yi alƙawarin cewa Afirka ta kudu za ta cire ka’idoji kan sanya hannun jari, tare da magance matsalolin da kamfanoni ke fuskanta na ƙasashen biyu.

A bayanin bayan taro da suka fitar ya nuna cewa, ƙasashen biyu sun ƙarƙare tattaunawar kan yarjejeniyar shekaru 5 ta musayar bayanai akan matsaloli na aikata manyan laifuka, barazanar tayar da hatsaniya, da kuma cin zarafi ƴa ƴan ƙasashen.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 17 hours 16 minutes 10 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 18 hours 57 minutes 35 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com