Home General Ina neman afuwa kan goyon bayan ƙudurorin haraji – Kofa

Ina neman afuwa kan goyon bayan ƙudurorin haraji – Kofa

Ɗan majalisar wakilai, mai wakiltar Ƙiru da Bebeji na jihar Kano, Abdulmumin Jibrin Kofa ya ce ba ɗari bisa ɗari yake goyon bayan ƙudurorin gyara haraji ba, sannan ya ƙara da cewa yana bayar da haƙuri.

Kofa ya bayyana haka a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook a yammacin ranar Laraba, inda a ciki ya ce, “babu wurin da ko sau ɗaya na ce ina goyon bayan sababbin dokokin haraji ɗari bisa ɗari.”

A cewarsa, “Abin da na ce (shi ne) akwai batutuwa da dama waɗanda za su zama alheri ga yankin arewa da ma Najeriya. Kuma mu ƴan majalisa na yankin arewa mu yi amfani da rinjayen da muke da shi a majalisa mu yi tsayin-daka mu goyi bayan duk wasu ƙudurorin da za su amfani arewa ta fannonin bunƙasa tattalin arzikin yankinmu da suke cikin kudurorin. Sannan mu kuma cire waɗanda za su cutar da mu, ko mu gyara su ta yadda ba za su cutar da mu ba.”

A cikin rubutun ya ƙara da cewa yana so ne yankin arewa su yi amfani damar dokar wajen bijiro da wasu sabbin hanyoyi, “mu shigar da su a cikin kundin ƙudirorin,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa, “ban taɓa ba, kuma ba zan taɓa goyon bayan duk wata doka ko ƙudirin da zai kawo illa ga mazaɓa ta, jihata ko Arewa da ma Najeriya ba.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp