Home General Nijeriya da Afirka ta kudu sun sake kulla kyakkayawar alaka

Nijeriya da Afirka ta kudu sun sake kulla kyakkayawar alaka

kasashen Najeriya da Afirka ta kudu sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyin haɗin gwiwa a ɓangaren kasuwanci, tattalin arziƙi da kuma tsaro, inda shugaba Cyril Ramaphosa ya amince da fara bai wa ƴan Najeriya musamman ƴan kasuwa damar samun bizar ƙasar ta shekaru 5, ba tare da nuna fasfo ba.

Ramaphosa ya bayyana wannan mataki a matsayin wani ɓangare na ƙara ƙarfafa alaƙa tsakanin Najeriya da Afrika ta Kudu, lokacin buɗe taron hukumar haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da Afirka ta Kudu karo na 11 a birnin Cape Town na ƙasar .

Shugaba Ramaphosa ya ce hakan zai sauƙaƙa tafiye-tafiyen ƴan kasuwa da masu yawon buɗe ido zuwa ƙasar, ta hanyar samun bizar shekaru 5 fiye da sau 1.

Cyril ya yi alƙawarin cewa Afirka ta kudu za ta cire ka’idoji kan sanya hannun jari, tare da magance matsalolin da kamfanoni ke fuskanta na ƙasashen biyu.

A bayanin bayan taro da suka fitar ya nuna cewa, ƙasashen biyu sun ƙarƙare tattaunawar kan yarjejeniyar shekaru 5 ta musayar bayanai akan matsaloli na aikata manyan laifuka, barazanar tayar da hatsaniya, da kuma cin zarafi ƴa ƴan ƙasashen.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp