Home General Majalisar dattijan Najeriya ta jingine tattaunawa kan ƙudurin haraji

Majalisar dattijan Najeriya ta jingine tattaunawa kan ƙudurin haraji

Majalisar dattijan Najeriya ta sanar da jingine tattaunawa kan ƙudurin sauye-sauye ga dokar haraji ta ƙasar, wadda shugaban ƙasar Bola Tinubu ya gabatar mata.

Majalisar ta ɗauki wannan matsaya ce a yau Laraba a lokacin muhawararta a zauren majalisar da ke Abuja.

Hakan na zuwa ne kwana ɗaya bayan da gwamnatin ƙasar ta umarci ma’aikatar shari’a ta ƙasar ta yi aiki tare da Majalisar Dokokin domin samun masalaha kan wasu ɓangarori na dokar da ake taƙaddama a kai.

Tattaunawa kan ƙudurin ya janyo zazzafar muhawara a faɗin Najeriya, yayin da wasu ɓangarorin ƙasar suka yi zargin cewa an cusa wasu abubuwa da za su cutar da wasu yankunan ƙasar.

A yanzu Majalisar ta umarci kwamitin da ta miƙa wa ƙudurin da ya jingine duk wani nazari a kansa, yayin da aka kafa wani kwamiti wanda zai yi aiki tare da ma’aikatar shari’a ta ƙasar domin duba ɓangarorin ƙudurin da ake taƙaddama a kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp