Home General Majalisar dattijan Najeriya ta jingine tattaunawa kan ƙudurin haraji

Majalisar dattijan Najeriya ta jingine tattaunawa kan ƙudurin haraji

Majalisar dattijan Najeriya ta sanar da jingine tattaunawa kan ƙudurin sauye-sauye ga dokar haraji ta ƙasar, wadda shugaban ƙasar Bola Tinubu ya gabatar mata.

Majalisar ta ɗauki wannan matsaya ce a yau Laraba a lokacin muhawararta a zauren majalisar da ke Abuja.

Hakan na zuwa ne kwana ɗaya bayan da gwamnatin ƙasar ta umarci ma’aikatar shari’a ta ƙasar ta yi aiki tare da Majalisar Dokokin domin samun masalaha kan wasu ɓangarori na dokar da ake taƙaddama a kai.

Tattaunawa kan ƙudurin ya janyo zazzafar muhawara a faɗin Najeriya, yayin da wasu ɓangarorin ƙasar suka yi zargin cewa an cusa wasu abubuwa da za su cutar da wasu yankunan ƙasar.

A yanzu Majalisar ta umarci kwamitin da ta miƙa wa ƙudurin da ya jingine duk wani nazari a kansa, yayin da aka kafa wani kwamiti wanda zai yi aiki tare da ma’aikatar shari’a ta ƙasar domin duba ɓangarorin ƙudurin da ake taƙaddama a kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp