Home General Hukumar alhazan Kano ta nuna damuwa kan rashin sayen kujerun aikin Hajjin...

Hukumar alhazan Kano ta nuna damuwa kan rashin sayen kujerun aikin Hajjin bana

Shugaban hukumar alhazan jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya nuna damuwarsa kan ƙarancin sayen kujerun aikin Hajji mai zuwa.

Shugaban ya bayyana hakan ne a yau Talata yayin wani taron haɗin gwiwa tsakanin ma’aikatan hukumar da da kuma manyan jami’anta na ƙananan hukumomi, a ofishin hukumar da ke Kano, kamar yadda wata sanarwa da kakakin hukumar Sulaiman A. Dederi ya fitar ta bayyana.

Alhaji Lamin ya buƙaci shugabannin hukumar na ƙananan hukumomi da su tashi haiƙan su ƙara azama wajen ganin an sayar da yawan kujerun da aka ware wa yankunansu.

Haka kuma ya yi kira da a samar da dabaru na bunƙasa cinikin kujerun da cimma aikin da ke gaban jihar a kan lokaci.

Hukumar alhazan ta sanya ranar 1 ga watan Janairu na shekara mai kamawa, 2025, a matsayin ranar rufe karɓar kuɗin ajiya na aikin Hajjin na bana daga maniyyata a jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp