Home General Jihohi biyu ne kaɗai za su amfana da sabuwar dokar harajin Najeriya...

Jihohi biyu ne kaɗai za su amfana da sabuwar dokar harajin Najeriya – Zulum

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya bayyana dalilin da ya sa gwamnonin Arewa suka shawarci shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya ɗan dakata kafin ya tura daftarin dokar sake fasalin harajin ƙasar zuwa majalisar dokoki.

Gwamnan wanda ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da gidan Talabijin na Channels ranar Lahadin da ta gabata, ya ce ƙungiyar gwamnonin Arewa na buƙatar lokaci ne domin tuntuɓa da kuma nazarin ɓangarorin dokar harajin.

“A kan wannan dokar, akwai abubuwa da dama da ba a fahimta ba. Mun duba tanadin da aka yi wa harajin VAT a cikin dokar. Bisa kididdigar da muka yi, Jihohin Legas da Ribas ne kaɗai za su ci gajiyar waɗannan sauye-sauyen. Mun yi namu binciken kuma mun gano cewa za mu yi asara,” inji Zulum.

“Me yasa muke hanzari? Mun shawarci Gwamnatin Tarayya da ta dakata, ta yi kakkaɓe wasu abubuwan da za su iya cutar da yankin Arewacin Najeriya.”

Zulum ya yi bayanin cewa idan har dokar ta sami amincewar Majalisar Dokoki ta kasa, za a cutar da jihohi da dama domin jihar Legas ce kaɗai za ta ci gajiyar wannan manufa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp