Home General Jihohi biyu ne kaɗai za su amfana da sabuwar dokar harajin Najeriya...

Jihohi biyu ne kaɗai za su amfana da sabuwar dokar harajin Najeriya – Zulum

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya bayyana dalilin da ya sa gwamnonin Arewa suka shawarci shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya ɗan dakata kafin ya tura daftarin dokar sake fasalin harajin ƙasar zuwa majalisar dokoki.

Gwamnan wanda ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da gidan Talabijin na Channels ranar Lahadin da ta gabata, ya ce ƙungiyar gwamnonin Arewa na buƙatar lokaci ne domin tuntuɓa da kuma nazarin ɓangarorin dokar harajin.

“A kan wannan dokar, akwai abubuwa da dama da ba a fahimta ba. Mun duba tanadin da aka yi wa harajin VAT a cikin dokar. Bisa kididdigar da muka yi, Jihohin Legas da Ribas ne kaɗai za su ci gajiyar waɗannan sauye-sauyen. Mun yi namu binciken kuma mun gano cewa za mu yi asara,” inji Zulum.

“Me yasa muke hanzari? Mun shawarci Gwamnatin Tarayya da ta dakata, ta yi kakkaɓe wasu abubuwan da za su iya cutar da yankin Arewacin Najeriya.”

Zulum ya yi bayanin cewa idan har dokar ta sami amincewar Majalisar Dokoki ta kasa, za a cutar da jihohi da dama domin jihar Legas ce kaɗai za ta ci gajiyar wannan manufa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp