Home General Sojoji kaɗai ba za su iya samar da tsaro a ƙasa ba...

Sojoji kaɗai ba za su iya samar da tsaro a ƙasa ba – Janar Chris Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya ce karfin soji kaɗai ba zai samar da tsaron da ake buƙata ba a Najeriya.

Ya ce amfani da karfin soji na bayar da gudummawar kashi 30 cikin ɗari ne kacal na tsaron ƙasa, yayin da kashi 70 ya dogara kan siyasa da kuma tallafi ga walwala da na tattalin arzikin al’umma.

Janar Musa ya bayyana haka ne a wani taro kan tsaron ƙasa da cibiyar daƙile ayyukan ta’addanci karkashin ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkar tsaro ya shirya a Abuja.

Babban hafsan ya buƙaci haɗin gwiwa wajen daƙile matsalar rashin tsaro a Najeriya.

“Dole ne a haɗa karfi da karfe wajen magance matsalar tsaro, musamman ganin rikice-rikice da kuma rashin tabbas da ya dabaibaye mutane,” in ji shi.

Ya ce mutane sun ɗauka cewa sojoji ne kaɗai za su samar da tsaro ba tare da la’akari kan irin gudummawar da kowane ɓangare zai bayar ba wajen tabbatuwar hakan.

Ya ƙara da cewa ƴan jarida ma na da rawar da za su taka wajen tabbatar da tsaro a faɗin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp