Home General Fararen hula 10,000 ne suka mutu a hannun sojojin Najeriya – Amnesty

Fararen hula 10,000 ne suka mutu a hannun sojojin Najeriya – Amnesty

Ƙungiyar kare hakkin ɗan’adam ta Amnesty International ta yi zargin cewa fararen hula kusan 10,000 ne suka mutu a hannun sojojin Najeriya, tun bayan fara yaƙi da ƙungiyar Boko Haram a arewa maso gabas.

Shugaban ƙungiyar ta Amnesty a Najeriya, Isa Sanusi, wanda ya bayyana haka a wani taron manema labarai a Maiduguri, ya kuma zargi Boko Haram da sojoji da laifukan take ƴancin ɗan’adam.

A cewarsa, dakarun soji sun take ƴancin bil’adama yayin gudanar da ayyukansu a yankin na arewa maso gabas.

Ya nuna takaicinsa kan yadda sojoji suka musanta hannunsu a lamarin bayan gabatar musu da rahoton da Amnesty ta yi kafin ta fitar da shi ga jama’a.

Sanusi ya ce tuni ƙungiyar ta shigar da ƙara gaban Kotun Duniya da ke Hague, kan zargin take ƴancin ɗan’adam a arewa maso gabas.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp