Home General Sojoji kaɗai ba za su iya samar da tsaro a ƙasa ba...

Sojoji kaɗai ba za su iya samar da tsaro a ƙasa ba – Janar Chris Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya ce karfin soji kaɗai ba zai samar da tsaron da ake buƙata ba a Najeriya.

Ya ce amfani da karfin soji na bayar da gudummawar kashi 30 cikin ɗari ne kacal na tsaron ƙasa, yayin da kashi 70 ya dogara kan siyasa da kuma tallafi ga walwala da na tattalin arzikin al’umma.

Janar Musa ya bayyana haka ne a wani taro kan tsaron ƙasa da cibiyar daƙile ayyukan ta’addanci karkashin ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkar tsaro ya shirya a Abuja.

Babban hafsan ya buƙaci haɗin gwiwa wajen daƙile matsalar rashin tsaro a Najeriya.

“Dole ne a haɗa karfi da karfe wajen magance matsalar tsaro, musamman ganin rikice-rikice da kuma rashin tabbas da ya dabaibaye mutane,” in ji shi.

Ya ce mutane sun ɗauka cewa sojoji ne kaɗai za su samar da tsaro ba tare da la’akari kan irin gudummawar da kowane ɓangare zai bayar ba wajen tabbatuwar hakan.

Ya ƙara da cewa ƴan jarida ma na da rawar da za su taka wajen tabbatar da tsaro a faɗin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp