Home General Shalkwatar tsaron Najeriya ta yi martana kan rahoton Amnesty

Shalkwatar tsaron Najeriya ta yi martana kan rahoton Amnesty

Shalkwatar tsaron Najeriya ta musanta zargin da ƙungiyar kare haƙƙin bil-adama ta Amnesty International, ta yi cewa mutum 10,000 ne suka mutu a hannun sojojin, tun bayan ɓarkewa rikicin Boko Haram a arewa maso gabashin Najeriya.

Daraktan ƙungiyar Amnesty a Najeriya, Mallam Isa Sanusi ne bayyana zargin sojojin da hannu a mutuwar mutanen da sauran nau’ikan cin zarafi, a wani jawabi da ya yi a tarin manema labarai a birnin Maiduguri.

Isa Sanusi a ce tuni ƙungiyarsu ta shigar da ƙara gaban kotun hukunta manyan laifuka ta ICC da ke birnin Hague kan zarge-zarge take haƙƙin ɗan’adam da take yi wa sojojin a yankin arewa maso gabashin ƙasar.

To sai dai yayin da take mayar da martani shalkwatar tsaron ƙasar, cikin wata sanarwa da kakakinta, Manjo Janar Edward Buba ya fitar ranar Juma’a ya bayyana zarge-zargen da masu tayar da hankali, kuma marasa tushe, kuma marasa hujja’.

”Duk da cewa yaƙin da sojoji ke yi a yankin Arewa maso gabashin Najeriya mai sarƙaƙiya ne cike da ƙalubale, muna bin ƙa’idojin da suka kamata. A duk lokacin da muka kama waɗanda ake zargi bayan ɗaukar bayanansu, mukan miƙa su hannun hukumomin da ya kamata domin a sake su ko a gurfanar da su a gaban kotu,” in ji Manjo Janar Edward Buba.

Sanarwar ta kuma ce shalkwatar tsaron ta gayyaci ƙungiyar ta Amesty zuwa ofishinta domin tabbatar da zarge-zargen.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp