Home General NNPCL na gudanar da jarrabawar ɗaukar ma’aikata

NNPCL na gudanar da jarrabawar ɗaukar ma’aikata

Babban kamfanin mai na Najeriya NNPCL na gudanar da jarrabawar ɗaukar sabbin ma’aikata.

Cikin wani saƙo da kamfanin ya wallafa a shafinsa na X, ya ce kimanin mutum 45,689 ne suke gudanar da jarrabawar wadda aka yi da kwamfuta.

”A yau NNPCL ya fara gudanar da jarrabawar ɗaukar ma’aikata da ake gudanarwa ta hanyar kwamfuta a cibiyoyi da dama a faɗin ƙasar nan”, in ji sanarwar.

NNPCL ya bayyana tsarin ɗaukar ma’aikatan da cewa tsari ne da yake gudanarwa a bayyane domin bai wa kowa dama.

”Domin damawa a kowa wajen ɗaukar aiki, NNPCL ya yi tanadi na musamman domin tabbatar da masu lalurar buƙata ta musamman da ke cikin masu neman aikin, sun samu damar gudanar da jarrabawar ba tare da wata matsala ba”, kamar yadda kamfanin ya wallafa a shafinsa na X

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp