Home General Tinubu ya taya Mahama murnar samun nasarar zaɓen Ghana

Tinubu ya taya Mahama murnar samun nasarar zaɓen Ghana

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya taya ɗan takarar shugaban ƙasar Ghana na jam’iyyar NDC mai hamayya, John Dramani Mahama, murnar nasarar da ya samu a zaɓen ƙasar.

Wannan na zuwa ne bayan da mataimakin shugaban ƙasa Muhammadu Bawumia ya amince da shan kaye.

Wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar, ta ce shugaba Tinubu ya yi fatan cewa hulɗa tsakanin ƙasashen biyu za ta ƙaru da kuma ganin kwanciyar hankali a faɗin ƙasashen ƙungiyar Ecowas.

Tinubu ya jinjinawa ƴan Ghana ta yadda suka fito suka yi zaɓe, inda a ɗaya gefen ya kuma yaba wa halin dattako da Bawumia ya nuna na amsa shan kaye tun kafin hukumar zaɓen Ghana ta sanar da sakamakon.

Har yanzu dai hukumar zaɓen ƙasar ba ta fara bayyana sakamakon zaɓen a hukumance ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp