Home General Sanatocin yankin Igbo sun nemi a sake duba ƙudurin haraji na Tinubu

Sanatocin yankin Igbo sun nemi a sake duba ƙudurin haraji na Tinubu

Sanatocin yankin kudu maso gabas sun shiga sahun waɗanda suke kira da a sake duba ƙudurorin haraji da shugaba Tinubu ya aika majalisa.

Jagoran gamayyar santocin yankin, Sanata Enyinnaya Abaribe (ɗan jam’iyyar APGA, mai wakiltar Abia ta kudu) ne bayyana hakan ga manema labarai bayan taron sanatocin daga jihohi biyar na yankin kudu maso gabas a ofishinsa.

Abaribe ya ce sanatocin yankin ba suna cewa a yi watsi da ƙudurorin ba ne, suna so a faɗaɗa tattaunawa, sannan a samu ƙarin lokaci domin su samu damar ganawa da waɗanda suke wakilta da sauran masu ruwa da tsaki kafin a ɗauki wani mataki a game da ƙudurorin.

Ya ƙara da cewa, “mun yi nazarin ƙudurorin sosai, sannan mun yanke shawarar cewa akwai buƙatar mu ƙara tattaunawa da dukkan masu ruwa da tsaki daga yankin kudu maso gabas. Muna so yi hakan ne domin tabbatar da cewa ƙudurorin sun yi amfani ga ƴan Najeriya, musamman yankinmu,” in ji Abaribe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp