Home General Jami’an DSS ba su da hurumin bincikar jakunkuna a filin jirgi –...

Jami’an DSS ba su da hurumin bincikar jakunkuna a filin jirgi – Festus Keyamo

Ministan harkokin Jiragen Sama da kula Sararin Samaniya, Festus Keyamo, ya bayyana cewa Hukumar Tsaro ta DSS ba ta da hurumin bincikar jakunkuna a filayen jiragen saman Najeriya.
ya bayyana hakan ne ta cikin shirin The Morning Show na Arise News TV a ranar Lahadi, Keyamo ya yi bayani kan sabbin matakai da aka dauka don rage tsangwama ga fasinjoji da kuma saukaka tsaro a filayen jiragen sama.
ya kuma ambaci wannan dabi’ar a matsayin wata ta’ada da ba ta da amfani kuma ba ta cikin aikace-aikacen da hukumar ke da alhakin su kai tsaye.
Ya jaddada cewa DSS ya kamata ta mayar da hankali kan bincikar mutanen da za su iya zama barazana ga tsaro, musamman ma waɗanda ke tafiya zuwa ƙasashen waje, maimakon gudanar da binciken kayan jakunkuna, wanda ba ya cikin manyan ayyukanta.
“DSS, ba ku da hurumin bincikar jakunkunan mutane. Ku mayar da hankali kan bincikar mutane da ke fita daga ƙasar,” in ji Keyamo.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp