Home General Za mu biya kudaden daliban Kano da Ganduje ya gaza biya a...

Za mu biya kudaden daliban Kano da Ganduje ya gaza biya a Cyprus – Gwamna Abba

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya dauki matakin magance matsalolin da daliban Kano wadanda gwamnatin Ganduje ta tura karatu kuma suka kasa karbar shaidar kammala karatunsu.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria a ranar Litinin, ta bayyana cewa gwamna Yusuf ya yi wata muhimmiyar ganawa da mahukuntan jami’ar Near East da ke Cyprus domin shawo kan lamarin.

Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan batun bayar da satifiket ga daliban Kano da suka kammala karatunsu a shekarar 2015 zuwa 2019.

Da yawa daga cikin wadannan daliban da aka yaye, musamman wadanda suka yi karatu a fannonin aikin likitanci da aikin jinya, sun kasa samun damar yin aikin da suka koya, sakamakon gaza biyan kudin makaranta da gwamnatin Ganduje ta yi.

Gwamnan ya bayyana lamarin a matsayin babban koma-baya, ba wai ga daliban da abin ya shafa ba, har ma da jihar, wadda take da bukatar kwararru jami’an kula da lafiya.

Gwamnana Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnatinsa zata biya duk kudaden da ake bin daliban domin su karɓi Satifiket dinsu don su fara amfani da abun da suka koya domin amfanin al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp