Home AFIRKA Ƴan bindiga sun hallaka fararen hula 21 a yammacin Jamhuriya Nijar

Ƴan bindiga sun hallaka fararen hula 21 a yammacin Jamhuriya Nijar

Akalla fararen hula 21 ƴan bindiga suka kashe a ranar asabar da ta wuce yayin wani hari da suka kai kan wata mota sufurin fasanja a yankin Tera da ke Jihar Tillabery  a yammacin Jamhuriya Nijar, kamar yadda gidan talabijin ɗin ƙasar ya sanar.

A rahoton mako-mako da ma’aikatar tsaron ƙasar ta saba fitarwa, gwamnatin ta ce an kai harin ne da misalin  ƙarfe 5 na yammacin rana  asabar daidai  lokacin da kasuwar kauyen ke tsaka da ci,  abunda ya sa aka samu asarar rayukan fararen hula da dama.

Rahoton ya ƙara da cewa ko a ranar Juma’a da ta gabata sai da dakarun ƙasar biyu suka mutu  bayan da ayirin motocinsu ya taka wani abun fashewa da aka dana a kauyen Tiyawa duk dai a Jihar ta Tillabery.

Da ya ke jagorantar  zana’izar waɗanda suka mutu a harin, gwamnan Jihar Tillabery Kanal Maina Bukar ya jajintawa iyalansu da sunan gwamnati, tareda fatan samun lafiya ga waɗanda sukaji rauni.

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da dakarun ƙasar ke ƙara kaimi wajan fatattakar ƴan bindiga da ke addabar jama’a a wanan yankin da yaraba iyaka da ƙasashen Mali da Burkina.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp