Home AFIRKA Ƴan bindiga sun hallaka fararen hula 21 a yammacin Jamhuriya Nijar

Ƴan bindiga sun hallaka fararen hula 21 a yammacin Jamhuriya Nijar

Akalla fararen hula 21 ƴan bindiga suka kashe a ranar asabar da ta wuce yayin wani hari da suka kai kan wata mota sufurin fasanja a yankin Tera da ke Jihar Tillabery  a yammacin Jamhuriya Nijar, kamar yadda gidan talabijin ɗin ƙasar ya sanar.

A rahoton mako-mako da ma’aikatar tsaron ƙasar ta saba fitarwa, gwamnatin ta ce an kai harin ne da misalin  ƙarfe 5 na yammacin rana  asabar daidai  lokacin da kasuwar kauyen ke tsaka da ci,  abunda ya sa aka samu asarar rayukan fararen hula da dama.

Rahoton ya ƙara da cewa ko a ranar Juma’a da ta gabata sai da dakarun ƙasar biyu suka mutu  bayan da ayirin motocinsu ya taka wani abun fashewa da aka dana a kauyen Tiyawa duk dai a Jihar ta Tillabery.

Da ya ke jagorantar  zana’izar waɗanda suka mutu a harin, gwamnan Jihar Tillabery Kanal Maina Bukar ya jajintawa iyalansu da sunan gwamnati, tareda fatan samun lafiya ga waɗanda sukaji rauni.

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da dakarun ƙasar ke ƙara kaimi wajan fatattakar ƴan bindiga da ke addabar jama’a a wanan yankin da yaraba iyaka da ƙasashen Mali da Burkina.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp