Home General Tinubu na son ganin babu wanda ya kwana da yunwa a Najeriya...

Tinubu na son ganin babu wanda ya kwana da yunwa a Najeriya – Minista

Shugaban kasar Bola Tinubu, ya ce samar da abinci shi ne babban abin da gwamnatinsa tafi ba wa muhimmanci.

Karamin ministan noma na kasar, Aliyu Abdullahi, ne ya bayyana hakan inda yace tun bayan da aka rantsar da shugaba Tinubu a watan Mayun 2023, gwamnatinsa ta bullo da shirye-shirye da dama domin tabbatar da an wadata kasar da abinci.

Cikin wata hira da gidan talbijin na Sunrise Daily ya yi da ministan, ya ce a cikin shirye-shirye Tinubu, samar da abinci shi ne kan gaba haka kuma bunkasa aikin noma ma na cikin manyan muradun shugaban kasar saboda baya ga samar da abinci da bangaren noma zai yi zai kuma bunkasa tattalin arzikin kasa.

Aliyu Abdullahi, ya ce shugaba Tinubu, ya damu matuka da matsalar karancin abincin da ake fama da ita a kasa,inda ya ce a wasu lokutan shugaba Tinubun kan sanar da su cewa babban burinsa shi ne ya kai al’ummar Najeriya matsayin da babu wanda zai kwana da yunwa.

Hauhawar farashin kayan abinci da ake fama da ita a Najeriya a baya bayannan, ta jefa miliyoyin mutane cikin yunwa a Najeriya.

A wannan yanayi da ake ciki, gwamnatin tarayyar Najeriya ta bullo da wasu hanyoyi na saukaka rayuwa ciki har da rabon tallafin abinci ga miliyoyin ‘yan Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp