Home General Tinubu na son ganin babu wanda ya kwana da yunwa a Najeriya...

Tinubu na son ganin babu wanda ya kwana da yunwa a Najeriya – Minista

Shugaban kasar Bola Tinubu, ya ce samar da abinci shi ne babban abin da gwamnatinsa tafi ba wa muhimmanci.

Karamin ministan noma na kasar, Aliyu Abdullahi, ne ya bayyana hakan inda yace tun bayan da aka rantsar da shugaba Tinubu a watan Mayun 2023, gwamnatinsa ta bullo da shirye-shirye da dama domin tabbatar da an wadata kasar da abinci.

Cikin wata hira da gidan talbijin na Sunrise Daily ya yi da ministan, ya ce a cikin shirye-shirye Tinubu, samar da abinci shi ne kan gaba haka kuma bunkasa aikin noma ma na cikin manyan muradun shugaban kasar saboda baya ga samar da abinci da bangaren noma zai yi zai kuma bunkasa tattalin arzikin kasa.

Aliyu Abdullahi, ya ce shugaba Tinubu, ya damu matuka da matsalar karancin abincin da ake fama da ita a kasa,inda ya ce a wasu lokutan shugaba Tinubun kan sanar da su cewa babban burinsa shi ne ya kai al’ummar Najeriya matsayin da babu wanda zai kwana da yunwa.

Hauhawar farashin kayan abinci da ake fama da ita a Najeriya a baya bayannan, ta jefa miliyoyin mutane cikin yunwa a Najeriya.

A wannan yanayi da ake ciki, gwamnatin tarayyar Najeriya ta bullo da wasu hanyoyi na saukaka rayuwa ciki har da rabon tallafin abinci ga miliyoyin ‘yan Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp