Home General Za a fuskanci hazo tsawon kwanaki uku a sassan Najeriya – NIMET

Za a fuskanci hazo tsawon kwanaki uku a sassan Najeriya – NIMET

Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya, NIMET, ta yi hasashen cewa za a fuskanci yanayin hazo da kura a sassan Najeriya daga yau Litinin zuwa Laraba.

Hukumar ta ce yankunan Arewacin dama na tsakiyar Najeriya ne za su fi fuskantar yanayin na hazo da da kura.

NIMET, ta ce za a samu matsala wajen hangen nesa saboda hazon a tsawon kwanakin ukun.

Daga nan hukumar ta bukaci jama’ar da ke zaune yankunan da hazon zai fi tsanani da su dauki matakan kariya musamman wadanda ke fama da wata lalura data shafi rashin kura ko hazo kamar Asma ko kuma cutukan da suka shafi numfashi.

Kazlaika NIMET, ya shawarci kamfanonin jiragen sama da ke zirga-zirga a Najeriya da su tabbata sun samu cikakken rahoton game da yanayin da za a iya kasancewa da shi a iya kwanakin da aka hasashen fuskantar hazo da kurar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp