Home General Ku yi koyi da demukradiyyar Ghana – Tinubu ga ECOWAS

Ku yi koyi da demukradiyyar Ghana – Tinubu ga ECOWAS

Shugaba Bola Tinubu ya buƙaci shugabannin ƙungiyar ƙasashen Afirka ta Yamma Ecowas, da su yi koyi tsarin dimokraɗiyyar Ghana, bayan gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da kuma na ƴan majalisar dokoki a ƙasar cikin lafiya da kwanciyar hankali.

An sake zaɓar John Mahama, tsohon shugaban ƙasar a zaɓen ranar 7 ga watan Disamba, inda ya kayar da mataimakin shugaban ƙasar Mahamudu Bawumia. Bawumia ya kira shi tare da yi masa murna tun kafin a sanar da sakamakon zaɓen a hukumance.

Da yake jawabi a wajen taron shugabannin ƙungiyar Ecowas karo na 66 da aka yi a Abuja yau Lahadi, Tinubu ya ce abin da ya faru a Ghana abin koyi ne ga wasu ƙasashe da ke yankin.

Shugaban ƙungiyar ta Ecowas ya kuma yaba wa shugaban ƙasar Ghana mai ci, Nana Akufo-Addo, wanda ya halarci taron a karo na karshe a matsayinsa na shugaba, da irin namijin ƙoƙari wajen shirya sahihin zaɓe.

Tinubu ya kuma yaba wa Senegal ka gudanar da zaɓen ƴan majalisa cikin gaskiya da lumana.

Ya yi kiran haɗin kai tsakanin ƙasashe mambobin Ecowas, musamman wajen kare hakkin ƴan ƙasashensu da kuma samar musu da ababen more rayuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp