Home General Gwamnan Kano ya saka sunan Sagagi cikin sabbin kwamishinoni Jihar

Gwamnan Kano ya saka sunan Sagagi cikin sabbin kwamishinoni Jihar

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya aikewa majalissar dokokin jihar wasika mai dauke da sunayen mutane 6 da yake son nadawa a matsayin kwamishinoni domin neman amincewa.

Idan za a iya tunawa a makon da ya wuce gwamnan ya yiwa majalisar zartarwarsa garanbawul tare da sallamar wasu daga cikin su.

Shugaban Majalisar Alhaji Jibril Ismail Falgore shi ne ya karanta wasikar a yayin zaman majalisar na yau.

Wadanda gwamnan ya aike da sunan su sun hadar

1- Alh. Shehu Wada Sagagi

2- Alh. Abdulkadir Abdulsalam (AG)

3- Ibrahim A. Waiya

4- Dr. Isma’il Danmaraya

5- Dr Ghaddafi Sani Shehu

6- Dr. Dahir M. Hashim.

Majalissar ta bukace su, su bayyana a gaban ta a gobe talata da misalin karfe goma na safe domin tantance su.

Ga dai sunayen ma’aikatun da a yanzu haka ba su da kwamishinoni:

1.  Hukumar raya karkara

2. Ma’aikatar Kudi

3. Muhalli

4. Yada Labarai

5. Jin kai

6. Makamashi

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp