Home General Gwamnan Kano ya saka sunan Sagagi cikin sabbin kwamishinoni Jihar

Gwamnan Kano ya saka sunan Sagagi cikin sabbin kwamishinoni Jihar

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya aikewa majalissar dokokin jihar wasika mai dauke da sunayen mutane 6 da yake son nadawa a matsayin kwamishinoni domin neman amincewa.

Idan za a iya tunawa a makon da ya wuce gwamnan ya yiwa majalisar zartarwarsa garanbawul tare da sallamar wasu daga cikin su.

Shugaban Majalisar Alhaji Jibril Ismail Falgore shi ne ya karanta wasikar a yayin zaman majalisar na yau.

Wadanda gwamnan ya aike da sunan su sun hadar

1- Alh. Shehu Wada Sagagi

2- Alh. Abdulkadir Abdulsalam (AG)

3- Ibrahim A. Waiya

4- Dr. Isma’il Danmaraya

5- Dr Ghaddafi Sani Shehu

6- Dr. Dahir M. Hashim.

Majalissar ta bukace su, su bayyana a gaban ta a gobe talata da misalin karfe goma na safe domin tantance su.

Ga dai sunayen ma’aikatun da a yanzu haka ba su da kwamishinoni:

1.  Hukumar raya karkara

2. Ma’aikatar Kudi

3. Muhalli

4. Yada Labarai

5. Jin kai

6. Makamashi

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp