Home General Ku yi koyi da demukradiyyar Ghana – Tinubu ga ECOWAS

Ku yi koyi da demukradiyyar Ghana – Tinubu ga ECOWAS

Shugaba Bola Tinubu ya buƙaci shugabannin ƙungiyar ƙasashen Afirka ta Yamma Ecowas, da su yi koyi tsarin dimokraɗiyyar Ghana, bayan gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da kuma na ƴan majalisar dokoki a ƙasar cikin lafiya da kwanciyar hankali.

An sake zaɓar John Mahama, tsohon shugaban ƙasar a zaɓen ranar 7 ga watan Disamba, inda ya kayar da mataimakin shugaban ƙasar Mahamudu Bawumia. Bawumia ya kira shi tare da yi masa murna tun kafin a sanar da sakamakon zaɓen a hukumance.

Da yake jawabi a wajen taron shugabannin ƙungiyar Ecowas karo na 66 da aka yi a Abuja yau Lahadi, Tinubu ya ce abin da ya faru a Ghana abin koyi ne ga wasu ƙasashe da ke yankin.

Shugaban ƙungiyar ta Ecowas ya kuma yaba wa shugaban ƙasar Ghana mai ci, Nana Akufo-Addo, wanda ya halarci taron a karo na karshe a matsayinsa na shugaba, da irin namijin ƙoƙari wajen shirya sahihin zaɓe.

Tinubu ya kuma yaba wa Senegal ka gudanar da zaɓen ƴan majalisa cikin gaskiya da lumana.

Ya yi kiran haɗin kai tsakanin ƙasashe mambobin Ecowas, musamman wajen kare hakkin ƴan ƙasashensu da kuma samar musu da ababen more rayuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp