Home General Ku yi koyi da demukradiyyar Ghana – Tinubu ga ECOWAS

Ku yi koyi da demukradiyyar Ghana – Tinubu ga ECOWAS

Shugaba Bola Tinubu ya buƙaci shugabannin ƙungiyar ƙasashen Afirka ta Yamma Ecowas, da su yi koyi tsarin dimokraɗiyyar Ghana, bayan gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da kuma na ƴan majalisar dokoki a ƙasar cikin lafiya da kwanciyar hankali.

An sake zaɓar John Mahama, tsohon shugaban ƙasar a zaɓen ranar 7 ga watan Disamba, inda ya kayar da mataimakin shugaban ƙasar Mahamudu Bawumia. Bawumia ya kira shi tare da yi masa murna tun kafin a sanar da sakamakon zaɓen a hukumance.

Da yake jawabi a wajen taron shugabannin ƙungiyar Ecowas karo na 66 da aka yi a Abuja yau Lahadi, Tinubu ya ce abin da ya faru a Ghana abin koyi ne ga wasu ƙasashe da ke yankin.

Shugaban ƙungiyar ta Ecowas ya kuma yaba wa shugaban ƙasar Ghana mai ci, Nana Akufo-Addo, wanda ya halarci taron a karo na karshe a matsayinsa na shugaba, da irin namijin ƙoƙari wajen shirya sahihin zaɓe.

Tinubu ya kuma yaba wa Senegal ka gudanar da zaɓen ƴan majalisa cikin gaskiya da lumana.

Ya yi kiran haɗin kai tsakanin ƙasashe mambobin Ecowas, musamman wajen kare hakkin ƴan ƙasashensu da kuma samar musu da ababen more rayuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp