Home General Matatar man Dangote ta rage farashin man fetur zuwa ₦899

Matatar man Dangote ta rage farashin man fetur zuwa ₦899

Matatar mai ta Dangote ta ce ta rage farashin litar man fetir zuwa naira 899.50 gabanin bikin kirsimati da sabuwar shekara.

Kakakin matatar Anthony Chiejina, ya ce an rage farashin litar man ne domin rage tsadar sufuri ga jama’a, a lokacin shagulgulan ƙarshen shekara.

A cikin watan Nuwamba ma, matatar man mai zaman kanta ta rage farashin litar mai zuwa naira 970.

Ya ce “Domin samar da sauƙi kan sufuri a lokacin hutun ƙarshen shekara, matatar mai ta Dangote ta fara sayar da mai a kan ragin farashi. Daga yau za a riƙa sayar da man a kan naira 899.50 a kowacce lita, daga mtatar man tamu.”

Chiejina ya jaddada cewa matatar ta jajirce wajen tabbatar da ganin an samarwa jama’ar Najeriya man fetir mai inganci kuma cikin farashi marar tsada.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp