Home General PDP ta yi watsi da kasafin kudin 2025

PDP ta yi watsi da kasafin kudin 2025

Jam’iyyar PDP ta soki kasafin kuɗin da shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya gabatar wa majalisar dokokin ƙasar, wanda ta bayyana a matsayin wani abu da ”ba zai yiwu ba” kuma wanda ”babu gaskiya a ciki”.

Sakataren yaɗa labaran PDP Debo Ologunagba, a cikin wata sanarwa a kan kasafin kuɗin, ya ce kasafin kuɗin ya shafi abubuwan da za su ƙara jefa jama’a cikin ƙangin talauci da kuma matsalar tsaro.

Shugaba Tinubu ya gabatarda kasafin na 2025, na naira tiriliyan 49.7 ga majalisar dokokin Najeriya, inda ya sha alwashin bayar da fifiko ga ɓangaren da samar da ayyukan raya ƙasa da fannin kiwon lafiya da kuma ilimi.

Sai dai jam’iyyar PDP mai adawa a ƙasar ta ce gabatar da kasafin kuɗin ba wani abu bane illa alƙawurran da ba za a iya cikawa ba.

Jma’iyyar adawan da zargi gwamnatin shugaba Tinubu da gazawa wajen samar da muhimman abubuwan more rayuwa ga jama’ar ƙasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Rahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara NePantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama'a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a GombeMa’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’Tinubu na Neman Amincewar Majalisar Dattawa kan Sabon Rancen $516.3mGadon Mulkin Gombe: Wa Ke Jin Tsoron Tasirin Pantami Daga Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Masu Kera Makamai ba Bisa Ka'ida ba a Filato, Sun Kama Wadanda ake Zargi da Ta'addanci a NijarShin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami
X whatsapp