Home General Fannin tsaro ya samu kaso mafi yawa a kasafin 2025 da shugaba...

Fannin tsaro ya samu kaso mafi yawa a kasafin 2025 da shugaba Tinubu ya gabatar

Fannin tsaro da manyan ayyuka da lafiya da ilmi sun samu kaso mai yawa cikin kasafin kuɗin shekarar 2025 da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatarwa da haɗakar zauren majalisun dokokin Najeriya wanda ya kai naira tiriliyan 47.9

A jawabin da ya yi a zauren majalisar dokokin domin amincewa da shi, Tinubu ya ce an warewa bangaran tsaro naira tiriliyan 4.91.

Manyan ayyukan da za a yi a shekara mai zuwa kuwa an ware naira tiriliyan 4.06 sai fannin kiwon lafiya da aka warewa naira tiriliyan 2.4 sai kuma fannin ilmi da aka warewa tiriliyan 3.5.

Tinubu ya ce kasafin zai taimaka wurin rage tsadar rayuwa daga kashi 34.6 zuwa kashi 15 a shekarar 2025, kuma zai sanya farashin dalar Amurka ya sauka daga 1700 zuwa 1500.

A kasafin na 2025 shugaban ya ce ana sa ran haƙo ganga ɗanyan mai miliyan 2.06 a kowacce rana, za kuma a samu raguwar shigo da tataccen man fetur cikin Najeriya tare da samun ƙaruwar fitar da tatacccen man.

A yayin gabatar da kasafin kuɗin Tinubu ya godewa ƴan Najeriya bisa hadin kan da yake samu a sauye-sauyen da gwamnatinsa ke yi cikin watanni 18 da suka gabata.

Ya ƙara da cewa tattalin arziƙin ƙasar na murmurewa kuma gwamnatinsa za ta ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace don ci gaban tattalin arziƙi, kuma gwamnati ba za ta ja da baya ba kan matakan da take ɗauka.

A bangaran samar da abinci shugaban ya ce ba za su yi wasa wurin tabbatar da wadatar da ƙasar da abinci, kuma suna ɗaukar matakan tabbatar da cewa ƴan Najeriya ba sa kwana da yunwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp