Home General Fannin tsaro ya samu kaso mafi yawa a kasafin 2025 da shugaba...

Fannin tsaro ya samu kaso mafi yawa a kasafin 2025 da shugaba Tinubu ya gabatar

Fannin tsaro da manyan ayyuka da lafiya da ilmi sun samu kaso mai yawa cikin kasafin kuɗin shekarar 2025 da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatarwa da haɗakar zauren majalisun dokokin Najeriya wanda ya kai naira tiriliyan 47.9

A jawabin da ya yi a zauren majalisar dokokin domin amincewa da shi, Tinubu ya ce an warewa bangaran tsaro naira tiriliyan 4.91.

Manyan ayyukan da za a yi a shekara mai zuwa kuwa an ware naira tiriliyan 4.06 sai fannin kiwon lafiya da aka warewa naira tiriliyan 2.4 sai kuma fannin ilmi da aka warewa tiriliyan 3.5.

Tinubu ya ce kasafin zai taimaka wurin rage tsadar rayuwa daga kashi 34.6 zuwa kashi 15 a shekarar 2025, kuma zai sanya farashin dalar Amurka ya sauka daga 1700 zuwa 1500.

A kasafin na 2025 shugaban ya ce ana sa ran haƙo ganga ɗanyan mai miliyan 2.06 a kowacce rana, za kuma a samu raguwar shigo da tataccen man fetur cikin Najeriya tare da samun ƙaruwar fitar da tatacccen man.

A yayin gabatar da kasafin kuɗin Tinubu ya godewa ƴan Najeriya bisa hadin kan da yake samu a sauye-sauyen da gwamnatinsa ke yi cikin watanni 18 da suka gabata.

Ya ƙara da cewa tattalin arziƙin ƙasar na murmurewa kuma gwamnatinsa za ta ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace don ci gaban tattalin arziƙi, kuma gwamnati ba za ta ja da baya ba kan matakan da take ɗauka.

A bangaran samar da abinci shugaban ya ce ba za su yi wasa wurin tabbatar da wadatar da ƙasar da abinci, kuma suna ɗaukar matakan tabbatar da cewa ƴan Najeriya ba sa kwana da yunwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp