Home General Fannin tsaro ya samu kaso mafi yawa a kasafin 2025 da shugaba...

Fannin tsaro ya samu kaso mafi yawa a kasafin 2025 da shugaba Tinubu ya gabatar

Fannin tsaro da manyan ayyuka da lafiya da ilmi sun samu kaso mai yawa cikin kasafin kuɗin shekarar 2025 da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatarwa da haɗakar zauren majalisun dokokin Najeriya wanda ya kai naira tiriliyan 47.9

A jawabin da ya yi a zauren majalisar dokokin domin amincewa da shi, Tinubu ya ce an warewa bangaran tsaro naira tiriliyan 4.91.

Manyan ayyukan da za a yi a shekara mai zuwa kuwa an ware naira tiriliyan 4.06 sai fannin kiwon lafiya da aka warewa naira tiriliyan 2.4 sai kuma fannin ilmi da aka warewa tiriliyan 3.5.

Tinubu ya ce kasafin zai taimaka wurin rage tsadar rayuwa daga kashi 34.6 zuwa kashi 15 a shekarar 2025, kuma zai sanya farashin dalar Amurka ya sauka daga 1700 zuwa 1500.

A kasafin na 2025 shugaban ya ce ana sa ran haƙo ganga ɗanyan mai miliyan 2.06 a kowacce rana, za kuma a samu raguwar shigo da tataccen man fetur cikin Najeriya tare da samun ƙaruwar fitar da tatacccen man.

A yayin gabatar da kasafin kuɗin Tinubu ya godewa ƴan Najeriya bisa hadin kan da yake samu a sauye-sauyen da gwamnatinsa ke yi cikin watanni 18 da suka gabata.

Ya ƙara da cewa tattalin arziƙin ƙasar na murmurewa kuma gwamnatinsa za ta ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace don ci gaban tattalin arziƙi, kuma gwamnati ba za ta ja da baya ba kan matakan da take ɗauka.

A bangaran samar da abinci shugaban ya ce ba za su yi wasa wurin tabbatar da wadatar da ƙasar da abinci, kuma suna ɗaukar matakan tabbatar da cewa ƴan Najeriya ba sa kwana da yunwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Rahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara NePantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama'a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a GombeMa’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’Tinubu na Neman Amincewar Majalisar Dattawa kan Sabon Rancen $516.3mGadon Mulkin Gombe: Wa Ke Jin Tsoron Tasirin Pantami Daga Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Masu Kera Makamai ba Bisa Ka'ida ba a Filato, Sun Kama Wadanda ake Zargi da Ta'addanci a NijarShin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami
X whatsapp