Home General Tattalin arzikin Najeriya yana haɓaka – Tinubu

Tattalin arzikin Najeriya yana haɓaka – Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce matakan da suka ɗauka na inganta tattalin arzikin ƙasar sun fara haifar da ɗa mai ido.

Tinubu ya bayyana haka ne a cikin jawabin da ya gabatar a majalisar dokoki, inda ya ce, “gyare-gyaren da muka yi sun fara haifar da ɗa mai ido.

“Ƴan Najeriya sun kusa fara cin gajiyar ingantaccen tattalin arziki, Ƙasarmu tana samun ci gaba sosai a fagen tattalin arziki.”

Ya ƙara da cewa tattalin arzikin Najeriya ya inganta, inda a cewarsa ya haɓaka da kashi 3.46 a rubu’i na uku na shekarar 2024, daga kashi 2.54 a rubu’i na uku na shekarar 2023.

Sai dai shugaban majalisar dattawan Najeriya, Godswill Akpabio, ya yi kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya ja kunnen “ministocinsa masu taurin kai” waɗanda ba sa amsa gayyatar majalisar dokoki.

Akpabio ya ce bai kamata irin waɗannan ministocin su samu gurbi a gwamnatinsa ba.

Akpabio ya bayyana haka ne a ranar Laraba, a lokacin da shugaban ƙasar yake gabatar da kasafin kuɗin 2025.

“Waɗanda suke ƙin amsa gayyatar majalisar dokoki ba ƴansiyasa ba ne, don haka bai kamata su samu gurbi a gwamnatinka ba,” kamar yadda Akpabio ya bayyana wa Tinubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp