‘Yanmajalisar wakilan Najeriya sun tara miliyan 704.91 daga albashinsu don tallafa wa ‘yan ƙasa

‘Yanmajalisar Wakilan Najeriya za su gabatar wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu kuɗin da suka tara daga albashinsu domin ba da tasu gudummawar wajen rage wa ‘yan Najeriya tsadar rayuwa.

Kakakin Majalisa Tajudeen Abbas ne ya bayyana hakan yayin zaman majalaisar a yau Alhamis, yana mai cewa kuɗin sun kai naira miliyan 704.91.

Ya ce za su yi hakan ne a ranar 31 ga watan Disamban 2024. Tun a watan Yuli ne ‘yanmajalisar suka yi alƙawarin sadaukar da rabin albashinsu domin taimakawa saboda cire tallafin man fetur.

“Ina farin cikin shaida muku cewa zuwa yanzu mun tara naira N704,907,578.82,” in ji Tajudeen.

“A ranar 31 ga watan Disamba, zan jagoranci shugabannin majalisa domin kai wa shugaban ƙasa kuɗin da zimmar yin amfani da su wajen tallafa wa mabuƙata.”

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1464 days 20 hours 47 minutes 57 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1446 days 22 hours 29 minutes 22 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com